Skip to main content
TARIHIN SANA’AR BORI
Tarihi ya nuna cewa shi dai bori shi ne imanin Bahaushe na asali, domin kuwa kowace al’umma idan aka bi tushe ko asalinta za a tarar tana da wata hanyar da ta ke bi  don yarda da wani abu mai girma wanda suka dogarar da rayuwarsu akansa. Tun can asali ma a kan samu wadansu al’ummomi da suke bautar gumaka ko iskoki ko taurari ko wuta da sauransu.
Haka kuma tarihi ya nuna cewa kafin shigowar wasu bakin al’ummomi a kasar Hausa, Hausawa suna da addininsu na gargajiya.A sakamakon irin nazarce-nazarce da aka yi a baya dayawa daga cikin masana na nuna cewa tarihin bori shi ne addinin gargajiya na Hausawa kai har ma da wasu wadanda ba Hausawa ba.
A wani bincike da na yi na samu wani littafi mai suna ‘Dangantakar Al’ada Da Addini’   wanda a cikin littafin aka nuna irin dangantakar da ke tsakanin al’ada da addini, domin a cikin littafin an nuna cewar daya daga cikin addinin gargajiya na Hausawa shi ne Bori wato bautar iskokai.
Bori tsohuwar al’ada ce wurin Hausawa tun fil’azal, abin day a sa aka ce haka kuwa shi ne sun fara al’adun ne tun lokacin das u ke duk maguzawa ne kuma har yanzu da mafi yawancinsu musulmai ne bas u daina wannan al’adar ba.
A jawabin Dakta Alhaji Yusuf Mai tama Sule  (Dan Masanin Kano 1973) wanda sashen binciken Harsunan Najeriya Na Jami’ar Bayero Kano ya  yi bayani a kan tarihin bori cewa ‘Duk inda jama’a ko kabilu ko jinsi suka taru to lallai a samu wani addini wanda a cikinsa ne mutane ke neman ceto ko dogaro ko ilhama,kazalika su kan yi amfani da wannan addini domin neman sanin gaibi ko neman sauki da waraka daga wasu cututtuka. Kuma wannan yarda haka ta keg a wadanda suke bin addinin Allah daya ko bautawa wanin Allah, wannan yana yi mana bayani cewa harkar bori mutane sun danganta ta da Allah wanda daga baya ya zamo kamar aljannu  kawai ake bauta ma wa tare da tsafe-tsafe.
Hausawa sun dauka cewa banda mutane, duniya na cike da wasu boyayyun halittu ma su dabi’a irin ta mutane. Saboda haka su ke kiransu ‘mutanen boye’. Kamar  yadda aka fahimta su mutanen boye su  ne wadanda bayan zuwan addinin musulunci ake kiransu aljannu ko iskokai  kamar yadda Kur’ani ya bayyana a cikin sura ta 72 aya ta 1 zuwa ta 16,
 A takaice wannan shi ne tarihin al’adar bori a dan karamin bincike na. Da fatan za a sanar da ni idan an ga wani kuskure a cikin rubutun.
 Naku a kullum Mustapha Salmanu  Kofar Sauri Katsina 08037675446  mustaphasalmanu00@gmail.com

Comments

Popular posts from this blog

NAZARIN LITTAFIN KUL'BA NA 'BARNA NA UMARU 'DANJUMA KATSINA

NAZARIN DA SHARHIN LITTAFIN WASAN KWAIKWAYO (KULBA NA BARNA...) . -MAWALLAFI: UMARU DANJUMA KATSINA (KASAGI) SHEKARAR BUGAWA: 1979 SABUNTAWA: 1985; 2004; 2006; 2007 ISBN: 978-978-169-245-1 GABATARWA: 'KULBA NA BARNA...' littafin wasan kwaikwayo ne wanda ke kunshe da labarin wata yarinya 'yar makaranta mai suna Zaliha. Mahaifinta, Malam Bankami, mutumin kauye ne, ya rasu ya bar ta riko a hannun Kawunta da ke zaune a wani babban gari. Kawun nata, Malam Inuwa, ya so cika wasiyyar Mahaifin Zaliha na aurar da ita da zarar ta kammala makarantar firamare, har ba shi ma fatar ta ci jarabawar shiga babbar makaranta, kamar yadda yake cewa, . ''Ai da ma a cikin wasiyyar da ya bari, ya ce don Allah don Annabi idan Zaliha ta isa aure, in yi mata. Ya ce in aurar da ita ga duk wanda za ta samu zaman lafiya. Don haka ma nake fatar ka da Allah sa ta ci jarabawar nan ta zuwa makarantar 'yan mata.'' . Tuni dai har Malam Inuwa ya gama maganar auren Zaliha da iya...

ZANCEN KARSHE

AL'ADAR ZANCEN K'ARSHE    Masu iya magana kan ce 'darajar galan marfinsa haka kuma duk darajar girman tuwo sai an sa masa miya'. Sannan masana (addini da boko) sun tabbatar mana da cewar duk al'ummar da ta yada al'adarta, ko shakka babu wannan al'umma ta shiga garari (rud'ani).  'Zancen 'karshe' al'ada ce wadda ake gudanarwa a wani yanki na garin Katsina. Wannan al'adar na d'aya daga cikin al'adun auren Hausawa a wannan yanki. Ana gudanar da wannan al'ada ne a ranar daren daurin aure; wato ana gobe za a d'aura aure kenan, sannan ana yin zancen 'karshe ne da daddare. Yadda ake gudanar da wannan al'ada shi ne; A ranar daren daurin aure da safe zuwa marece za a sanar da abokanin ango inda za a had'u domin zancen 'karshe, ita ma ta 'bangaren amarya za a sanar da 'kawaye wurin da za a had'u domin zancen 'karshe. Kafin lokacin ya yi abokanin ango za su tanadi kayayyakin ma'kulashe kama...

KATSINA DISTRICT HEADS

1. Kauran Katsina Hakimin Rimi Alhaji Nuhu Abdulkadir. 2. Galadiman Katsina Hakimin Malumfashi Hon Justice Mamman Nasir GCFR (Rtd). 3. Yandakan katsina Hakimin Dutsinma Alhaji Sada Muhammad Sada. 4. Durbin Katsina Hakimin Jikamshi Alhaji Aminu Kabir Usman 5. Magajin Garin Katsina hakimin cikin Birni da Kewaye Alhaji Aminu Abdulmumin Kabir 6. Sarkin Maskan Katsina Hakimin Funtua Alhaji Sambo Idris Sambo 7. Sarkin Musawa Hakimin Musawa Alhaji Muhammadu Gidado Usman Liman 8. Kankiyan Katsina Hakimin kankia Alhaji Musa Hassan Sada. 9. Sarkin Sulluwan Katsina Hakimin kaita Alhaji Abdulkarim Kabir Usman. 10. Sarkin Shanun Katsina Hakimin Charanchi Alhaji Abashe Abdulkadir. 11. Sarkin Yamman Katsina Hakimin Faskari Alhaji Tukur Usman Sa’idu. 12. Sarkin Gabas din Katsina Hakimin Mani Alhaji Babani Isah Mani. 13. Sarkin Arewan Katsina Hakimin Jibia Alhaji Rabe Muhammad Rabiu. 14. Sarkin Kudun katsina Hakimin Danja Alhaji M T Bature. 15. Makaman Katsina Hakimin Bakori Alhaji ...