Skip to main content

Posts

Showing posts from April, 2019

NAZARIN LITTAFIN KUL'BA NA 'BARNA NA UMARU 'DANJUMA KATSINA

NAZARIN DA SHARHIN LITTAFIN WASAN KWAIKWAYO (KULBA NA BARNA...) . -MAWALLAFI: UMARU DANJUMA KATSINA (KASAGI) SHEKARAR BUGAWA: 1979 SABUNTAWA: 1985; 2004; 2006; 2007 ISBN: 978-978-169-245-1 GABATARWA: 'KULBA NA BARNA...' littafin wasan kwaikwayo ne wanda ke kunshe da labarin wata yarinya 'yar makaranta mai suna Zaliha. Mahaifinta, Malam Bankami, mutumin kauye ne, ya rasu ya bar ta riko a hannun Kawunta da ke zaune a wani babban gari. Kawun nata, Malam Inuwa, ya so cika wasiyyar Mahaifin Zaliha na aurar da ita da zarar ta kammala makarantar firamare, har ba shi ma fatar ta ci jarabawar shiga babbar makaranta, kamar yadda yake cewa, . ''Ai da ma a cikin wasiyyar da ya bari, ya ce don Allah don Annabi idan Zaliha ta isa aure, in yi mata. Ya ce in aurar da ita ga duk wanda za ta samu zaman lafiya. Don haka ma nake fatar ka da Allah sa ta ci jarabawar nan ta zuwa makarantar 'yan mata.'' . Tuni dai har Malam Inuwa ya gama maganar auren Zaliha da iya...