Skip to main content

ZANCEN KARSHE

AL'ADAR ZANCEN K'ARSHE
   Masu iya magana kan ce 'darajar galan marfinsa haka kuma duk darajar girman tuwo sai an sa masa miya'. Sannan masana (addini da boko) sun tabbatar mana da cewar duk al'ummar da ta yada al'adarta, ko shakka babu wannan al'umma ta shiga garari (rud'ani).

 'Zancen 'karshe' al'ada ce wadda ake gudanarwa a wani yanki na garin Katsina. Wannan al'adar na d'aya daga cikin al'adun auren Hausawa a wannan yanki. Ana gudanar da wannan al'ada ne a ranar daren daurin aure; wato ana gobe za a d'aura aure kenan, sannan ana yin zancen 'karshe ne da daddare.
Yadda ake gudanar da wannan al'ada shi ne; A ranar daren daurin aure da safe zuwa marece za a sanar da abokanin ango inda za a had'u domin zancen 'karshe, ita ma ta 'bangaren amarya za a sanar da 'kawaye wurin da za a had'u domin zancen 'karshe. Kafin lokacin ya yi abokanin ango za su tanadi kayayyakin ma'kulashe kamar su; goro, alewa, cakuleti, biskit da makamantansu. Bayan an tattaru a wurin da aka shelanta daman 'kawayen amarya sun yi shimfid'a a wannan wuri, za su zauna a gefe guda tare da amarya, su ma a 'bangaren abokan ango za su zauna a gefe guda suna masu juyowa suna kallon amare sannan ango na tare da su. A nan za a cigaba da hira, kusan kowa sai ya yi magana a wurin, idan da mai labari kuma ya bada, sannan daga baya sai 'kawayen amarya su rarraba wad'annan kayayyaki na ta'ba-ka-lashe, zai kasance ana hira ana tamna tare da tsotsa  wad'annan kaya. Haka za a cigaba da hira har sai duhu ya fara sannan a yi bankwana da juna a rabu cikin farin ciki da shau'kin rabuwa da juna.
Shin ko akwai inda ka san ana gudanar da wannan al'ada?.

Mustapha Salmanu


Comments

Popular posts from this blog

NAZARIN LITTAFIN KUL'BA NA 'BARNA NA UMARU 'DANJUMA KATSINA

NAZARIN DA SHARHIN LITTAFIN WASAN KWAIKWAYO (KULBA NA BARNA...) . -MAWALLAFI: UMARU DANJUMA KATSINA (KASAGI) SHEKARAR BUGAWA: 1979 SABUNTAWA: 1985; 2004; 2006; 2007 ISBN: 978-978-169-245-1 GABATARWA: 'KULBA NA BARNA...' littafin wasan kwaikwayo ne wanda ke kunshe da labarin wata yarinya 'yar makaranta mai suna Zaliha. Mahaifinta, Malam Bankami, mutumin kauye ne, ya rasu ya bar ta riko a hannun Kawunta da ke zaune a wani babban gari. Kawun nata, Malam Inuwa, ya so cika wasiyyar Mahaifin Zaliha na aurar da ita da zarar ta kammala makarantar firamare, har ba shi ma fatar ta ci jarabawar shiga babbar makaranta, kamar yadda yake cewa, . ''Ai da ma a cikin wasiyyar da ya bari, ya ce don Allah don Annabi idan Zaliha ta isa aure, in yi mata. Ya ce in aurar da ita ga duk wanda za ta samu zaman lafiya. Don haka ma nake fatar ka da Allah sa ta ci jarabawar nan ta zuwa makarantar 'yan mata.'' . Tuni dai har Malam Inuwa ya gama maganar auren Zaliha da iya...

KATSINA DISTRICT HEADS

1. Kauran Katsina Hakimin Rimi Alhaji Nuhu Abdulkadir. 2. Galadiman Katsina Hakimin Malumfashi Hon Justice Mamman Nasir GCFR (Rtd). 3. Yandakan katsina Hakimin Dutsinma Alhaji Sada Muhammad Sada. 4. Durbin Katsina Hakimin Jikamshi Alhaji Aminu Kabir Usman 5. Magajin Garin Katsina hakimin cikin Birni da Kewaye Alhaji Aminu Abdulmumin Kabir 6. Sarkin Maskan Katsina Hakimin Funtua Alhaji Sambo Idris Sambo 7. Sarkin Musawa Hakimin Musawa Alhaji Muhammadu Gidado Usman Liman 8. Kankiyan Katsina Hakimin kankia Alhaji Musa Hassan Sada. 9. Sarkin Sulluwan Katsina Hakimin kaita Alhaji Abdulkarim Kabir Usman. 10. Sarkin Shanun Katsina Hakimin Charanchi Alhaji Abashe Abdulkadir. 11. Sarkin Yamman Katsina Hakimin Faskari Alhaji Tukur Usman Sa’idu. 12. Sarkin Gabas din Katsina Hakimin Mani Alhaji Babani Isah Mani. 13. Sarkin Arewan Katsina Hakimin Jibia Alhaji Rabe Muhammad Rabiu. 14. Sarkin Kudun katsina Hakimin Danja Alhaji M T Bature. 15. Makaman Katsina Hakimin Bakori Alhaji ...